Home DUNIYA ECOWAS ta bukaci AU da ta amince da kudirorin da ta dauka...

ECOWAS ta bukaci AU da ta amince da kudirorin da ta dauka kan Nijar

Kungiyar Kasashen Yammacin Afrika ta ECOWAS ta umarci rundunarta da ke cikin shirin-ko-ta-kwana da ta maido da kundin tsarin mulki a Jamhuriyar Nijar.

Shugaban gudanarwar ECOWAS Omar Alie Touray ya bayyana haka a lokacin da yake karanta kudirorin da kungiyar ta dauka game da juyin mulkin Nijar a wani taro da ya gudana birnin Abuja na Najeriya a wannan Alhamis.

ECOWAS ta bayyana cewa, ta dauki matsayar ce bayan ta nazarci rahoto da kuma shawarwarin da Kwamitin Hafsosshin Tsaronta ya bayar, tana mai korafin cewa, daukacin hanyoyin diflomasiyar da ta bi don warware rikicin siyasar kasar sun ci-tura sakamakon yadda sojojin suka yi juyin mulki suka ki mutunta umarnin da aka ba su.

ECOWAS ta bai wa sojojin na Nijar wa’adin ranar 6 ga wannan wata na Agusta da su mayar da shugaba Mohamed Bazoum kan kujerarsa ta shugaban kasa, amma suka ki mutunta wannan umarni.

Yanzu haka ECOWAS ta jaddada matsayarta ta yin Allah-wadai da juyin mulkin gami da ci gaba da tsare shugaba Bazoum da iyalansa da wasu jami’an gwamnatinsa.

Kungiyar ta kasashen yammacin Afrika ta sanar da tsaurara matakan rufe kan iyakokin Nijar da haramta tafiye-tafiye da daskarar da kadarorin wadanda ke da hannu a juyin mulkin bayan ta gaza magance rikicin kasar ta hanyar laluma.

A bangare guda, ECOWAS ta bukaci Kungiyar AU da ta amince da daukacin kudirorin da ta dauka a dalilin halin da ake ciki a Jamhuriyar Nijar.

Har ila yau, ECOWAS ta yi kira ga kasashen duniya aminanta da Majalisar Dinkin Duniya da su mara mata baya domin samun natija ta gaggawa dangane da maido da kundin tsarin mulki a Nijar.

Kawo yanzu dai, sojojin da suka yi juyin mulkin na Nijar ba su nuna wata alamar shiga tattaunawar fahimtar juna da ECOWAS ba duk kuwa da tarin takunkuman da aka malkaya musu baya ga barazanar daukar matakin sojin da aka yi musu.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp