Home Labarai Emefiele ya cika ka’idar Beli

Emefiele ya cika ka’idar Beli

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya koma gida bayan ya cika sharuɗɗan belin da kotu ta ba shi.

Mai magana da yawun Gidan Yari na Kuje da ke Abuja, inda aka tsare Mista Emefiele, ya tabbatar da cewa an saki tsohon gwamnan a yammacin Juma’a.

Tun a ranar 22 ga watan Nuwamba ne Babbar Kotun Tarayya ta ba da belinsa kan naira miliyan 300 tare da gabatar da mutum biyu da ke da kadarori a unguwar Maitama da ke birnin na Abuja. Haka nan, kotun ta umarce shi da miƙa mata dukkan takardunsa na tafiye-tafiye.

Lamarin na zuwa ne bayan wani rahoto da mai bincke na musamman, Jim Obazee, ya zarge shi da karya dokar kwangila da sayen kayayyakin gwamnati.

Rahoton Obazee, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa a watan Yuli don ya binciki CBN a ƙarƙashin mulkin Emefiele, ya zarge shi da amfani da wakilansa wajen sayen Bankin Union, da kuma yin amfani da ƙarfin ikonsa a cinikin bankunan Polaris da Keystone.

Gwamnatin Tinubu na zargin tsohon gwamnan wanda ta dakatar a watan Yuni da aikata almundahanar kuɗi naira biliyan 1.2, zargin da ya musanta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp