Fashewar wani abu tayi sanadiyyar mutuwar yara 6 a jihar Borno

fashearwa wani abu yayi sandiyyar mutuwar wasu yara a shida a karamar hukumar Gubio, da ke jihar Borno a rewa maso gabashin Nijeriya.

rundunar ‘yan sandna jihar ta bakin kakakinta ASP Nahun Daso ta tabbatar da aukuwar lamarin inda ta ce fashewar ta faru ne a wani gini da ke makarantar Islamiyya a ranar Asabar.

rundunar ta ce an tara wasu kayayyakin gwan-gwan da aka yi rashin sa’a wasu matasa da suka je wajen suka taru, a nan ne kuma aka samu abubuwan fashewa da suka tashi.

Rahotanni sun ce yaran kan tara ƙarafa da kuma sayar wa al’ummar yankin.

Duk da haramcin da aka yi kan sana’ar gwan-gwan, har yanzu ana cinikin lalatattun karafa a yankin da ke fama da tashe-tashen hankula na masu tayar da ƙayar baya.

ASP Nahun ya ce suna wayar da kan mutane game da “na’urorin fashewa” tare da hana saye da sayar da kayan gwan-gwan. Ya kuma kara da cewa rundunarsu za ta yi bincike a kan lamarin.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 47 minutes 28 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 28 minutes 53 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com