Home Labarai Yadda ma’aikatan jinya da ungozoma suka gudanar da zanga-zanga a Abuja

Yadda ma’aikatan jinya da ungozoma suka gudanar da zanga-zanga a Abuja

Gwamman ma’aikatan jinya da ungozama ne suka hau titunan birnin Abuja domin nuna kin amincewarsu ga wasu sabbin dokoki da hukumar kula da ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa ta shimfida musu.

Sabbin dokokin dai sun hadar da kwashe shekaru biyu wadanda suka karanci aikin jinya a jami’a suna aiki a Najeriya kafin hukumar ta tantance su a matsayin kwararrun ma’aikatan jinya. Hukumar ta kuma kara kudin tantancewar daga dubu 29 zuwa dubu 300.

To sai dai kungiyar ma’aikatan jinyar ta ce kudin ya yi yawa kasancewar a cikinsu akwai wadanda suke daukar albashin da bai wuce naira dubu 50 ba a wata.

Ma’aikatan lafiya dai a Najeriya na yawan ficewa daga kasar da zarar sun samu lasisin aiki zuwa wasu kasashen ketare.

Sau da dama dai ma’aikatan lafiya a Najeriya na kokawa kan rashin isasshiyar kulawa da suke samu ciki har da albashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp