Home Labarai Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya ce ba shi da shirin kara farashin man fetur a kasar duk kuwa kara tabarbarewar darajar takardar kudin Naira da ya haddasa tsadar rayuwa.

Karo na biyu kenan da Najeriyar ke karya darajar kudinta cikin kasa da shekara guda, lamarin da ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki kari kan matsin rayuwar da jama’a ke fuskanta tun tuni, kuma wannan batu ya sanya fargabar karuwar farashin man na fetur, batun da kamfanin na NNPC ke cewa babu wannan shirin a yanzu.

Sanarwar ta NNPC na zuwa a dai dai lokacin da kiraye-kiraye ke ci gaba da tsananta daga kungiyoyi wajen ganin gwamnatin Najeriyar ta dauki matakan kawo sassauci kan matsin rayuwar da ake ciki, wadannan kungiyoyi kuwa har da na kwadago da suka bayar da wa’adin makwanni biyu ko kuma tsunduma yajin aiki.

A bangare guda kungiyar gwamnonin Najeriyar ta aikewa da gwamnatin tarayya bukatar gaggawa wajen magance matsalar ta tsadar rayuwa baya ga daidaita farashin Naira da kuma uwa uba magance matsalolin tsaron da arewacin kasar ke fama da shi.

A hukumance dai yanzu ana sayar da duk dalar Amurka guda kan Nairar Najeriyar dubu 1 da 531 sabanin 900 da ake sayarwa a makwannin baya, lamarin da ya sake tsawwala tsadar rayuwar da al’umma kef ama da shi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp