Home Labarai Janye Tallafin Lantarki ka iya jefa ‘yan Nijeriya mawuyacin hali

Janye Tallafin Lantarki ka iya jefa ‘yan Nijeriya mawuyacin hali

Al’ummar Najeriya za su fuskanci karin kudin lantarki muddin gwamnati ta ci gaba a kan shirinta na janye tallafi da kashi 15 cikin 100.

Yin hakan zai kara jefa al’ummar kasar cikin mawuyacin hali bisa la’akari da hakin da ake ciki na matsin tattalin arziki.

A ranar Talata ne mai magana da yawun shugaban kasar Bayo Onanuga ya sanar da shirin gwamnatin, yana mai cewa za a yi hakan ne domin a rage kashe kudaden gwamnati.

Idan aka dauki wannan mataki za a rage kashe kudaden gwamnati da kusan dala biliyan biyu da miliyan dari shida.

Ba dai a bayyana lokacin da gwamnati za ta janye tallafin kashi 15 cikin 100 ba.

Ko a yanzu ma ba kowa ba ne yake iya sayen wutar saboda yadda ta yi tsada duk da cewa farashin ya banbanta daga gari zuwa gari da kuma atsakanin unguwanni.

Cire wannan tallafi na nufin wuta za ta koma hannun ‘yan kasuwa kacokan. To sai dai har kawo yanzu kusan fiye da kaso 70 na ‘yan Najeriya ba su da mitar da ake sanyawa kudi.

A kwanakin baya ne dai asusun lamuni na duniya ya shawarci Najeriya da ta cire tallafin mai kacokan da kuma tallafin da take bai wa ‘yan kasar a wutar lantarki.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp