Kotun tarayya a jihar Kano ta dakatar da umarnin Kotu kan Ganduje

Babbar Kotun Tarayya dake zaman ta a Jihar Kano ta dakatar da umarnin Babbar Kotun Jihar Kano na Dakatar Da Ganduje daga Jam’iyyar APC.
Alƙalin Kotun mai Shari’a Justice A.M. Liman ne ya bada umarni biyo bayan ƙarar da Ganduje ya shigar a gaban kotun, inda ya yi ƙarar wasu ɓangarori 14, kamar yadda takardar Umarnin ta nuna.
tun da fari dai shugabancin Jam’iyyar APC na mazabar Ganduje dake karamar hukumar Dawakin Tofa ne ya bayar da tabbacin dakatar da Ganduje daga Jam’iyyar bisa abin da ya kira da zargin cin hanci da ake yi masa kuma ya kasa kare kanshi.
ko da yake shugabancin Jam’iyyar reshen jihar ta kano ya barrata jam’iyyar da wadanda suka yanke hukunci cewa ba ‘yan APC bane jam’iyyar adawa su yiwa aiki.
ko dai a ‘yan tsakanin na shugaban Jam’iyyar APCn na riko Abdullahi Ganduje ya fito ya bayyana cewa yana nan a shugabancin jam’iyyar ba gudu ba ja da baya tare da bukatar a hukunta alkalin da ya yanke hukuncin cewa shi ba dan Jam’iyyar APC bane.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 41 minutes 53 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 23 minutes 18 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com