Home DUNIYA Amurka na ganawa da gwamnatin Nijar kan janye dakarunta daga kasar

Amurka na ganawa da gwamnatin Nijar kan janye dakarunta daga kasar

Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar domin tattaunawa game da batun janye sojojinta daga Nijar ɗin.

Hakan ya zo sakamakon makonni da gamayyar ƙungiyar farar hula a Nijar ta shafe tana zanga-zangar goyon bayan juyin mulkin da aka yi a ƙasar ranar 26 ga watan Yuli.

“Jakadiyar Amurka a Nijar, Kathleen FitzGibbon da Manjo Janar Ken Ekman, Daraktan tsare-tsare da tattaunawa na rundunar tsaro ta Amurka da Afirka za su gana da mambobin Majalisar Tabbatar da Tsaron Ƙasa (CNSP) da ke Yamai,” in ji wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar.

A mako mai zuwa ne, wasu jami’an tsaron Amurka za su kai ziyara Yamai domin tsara yadda za a kwashe sojojin ƙasar cikin mutunci da gaskiya.

A cewar wata sanarwa, gwamnatin Amurka za ta ci gaba da goyon bayan al’ummar Nijar yayin da suke ƙoƙarin fatattakar mayaƙa.

Sanarwar ta kuma ce mataimakin sakataren harkokin waje, Kurt M. Campbell zai je Yamai a watanni masu zuwa domin tattauna batun yin haɗin gwiwa a batutuwan da buƙatarsu ta zo ɗaya.

Sojojin Nijar sun sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar tsaro da Amurka yayin da ƙasar ke ci gaba da fuskantar ƙaruwar matsalar tsaro da hare-hare daga ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

Magoya bayan gwamnatin sojoji a Nijar sun ce kasancewar sojoji har da na Amurka da Faransa ba ya tasiri ga tsaron ƙasar.

A yanzu, sojojin sun ƙulla yarjejeniya da Rasha, a wani mataki da zai faɗaɗa tasirin Moscwo a Afrika.

A makon da ya gabata ne, ƙwararrun sojojin Rasha suka isa Yamai domin horas da dakarun Nijar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp