Home Labarai ‘Yansanda a jihar Bauchi sun hallaka ‘yan Ta’adda takwas

‘Yansanda a jihar Bauchi sun hallaka ‘yan Ta’adda takwas

Ƴan sanda tare da haɗin gwiwar ƙungiyar mahauta a Bauchi sun kashe mutum takwas da ake zargin masu garkuwa da mutane ne yayin musayar wuta a kusa da iyakar jihar da Filato.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda ta jihar Bauchi SP Ahmed Wakil ya bayyana wa ƴan jarida a jihar a ranar Alhamis cewa ƴan sanda sun samu nasarar ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su don karɓar kuɗin fansa.

Sanarwa da mai magana da yawun hukumar ya fitar ta bayyana cewa “Jami’an na ƴan sanda da aka kawo daga offisoshin ƴan sanda na Gumau da Tilde da Tulu sun haɗu da masu garkuwa da mutane tare da makamansu yayin da suke bakin aikinsu na tabbatar da tsaro inda suka yi musayar wuta da ya yi sanadiyyar kashe masu garkuwar huɗu.

“Biyu daga cikin waɗanda ake zargin da suka mutu daga bisani sun amsa laifin garkuwa da mutane da dama a Bauchi da Filato da ya haɗa da mummunan kisan gillar da aka yi wa maigarin Ruruwai a garin Lame dake ƙaramar hukumar Toro.

“Yayin musayar bindiga tsakanin jami’an da sauran masu garkuwar da ke gadin mutanen da aka yi garkuwa da su aka sake kashe mutum huɗu cikinsu sannan aka samu ƙwato mutum ukun da ke hannunsu ba tare da biyan kuɗin fansa ba”.

SP Wakil ya yi kira ga al’umomin garuruwan Bauchi da su ba da haɗin kai da jami’an tsaron ta hanyar samar musu da bayanan sirri da za su taimaka wajen shawo kan matsalolin tsaro kafin ma su faru wanda faruwar tasu kan iya samar da mummunan lahani a kan rayuka da kuma dukiyoyi.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp