Home DUNIYA Amurka na shirin janye sojojinta daga Chadi

Amurka na shirin janye sojojinta daga Chadi

Amurka za ta janye wasu daga cikin dakarunta daga Chadi na wani ɗan lokaci, kwanaki bayan da ta amince ta janye duka dakarunta daga Nijar mai maƙwabtaka.

Sakataren yaɗa labarai na ma’aikatar tsaron Amurka Pentagon, Manjo Janar Pat Ryder ya ce Amurka za ta sakewa wasu daga cikin sojojin wuri daga Chadi amma bai ce suwa ne waɗanda matakin zai shafa ba ko kuma inda za a kai su.

“Wannan mataki ne na wucen gadi a yunƙurin sake nazari kan haɗin gwiwar tsaro da za a ci gaba da yinta bayan zaɓen shugaban ƙasar Chadi na ranar 6 ga watan Mayu.” kamar yadda ya bayyana.

Sanarwar ta zo ne bayan da shugaban hafsan sojin saman Chadi, a farkon watan nan, ya umarci Amurka ta dakatar da ayyukanta a sansanin sojin sama da ke N’Djamena, babban birnin Chadi, in ji kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Gen Ryder ya kuma ce an soma tattaunawa da sojojin da ke mulki a Nijar da majalisar tabbatar da tsaron ƙasa CNSP ranar Laraba domin tabbatar da janye sojojin Amurka daga ƙasar cikin lumana.

Amurka ta dogara kan Nijar a matsayin babbar sansaninta ta bibiyar ayyukan ƴan ta’adda a yankin Sahel.

Sai dai sojojin Nijar da ke mulkin ƙasar tun Yuli, sun kawo ƙarshen yarjejeniyar tsaro da ƙasar tare da korar sojojin Faransa, wani yunƙuri na yanke alaƙa da ƙasashen yamma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp