Home DUNIYA Amurka na shirin janye sojojinta daga Chadi

Amurka na shirin janye sojojinta daga Chadi

Amurka za ta janye wasu daga cikin dakarunta daga Chadi na wani ɗan lokaci, kwanaki bayan da ta amince ta janye duka dakarunta daga Nijar mai maƙwabtaka.

Sakataren yaɗa labarai na ma’aikatar tsaron Amurka Pentagon, Manjo Janar Pat Ryder ya ce Amurka za ta sakewa wasu daga cikin sojojin wuri daga Chadi amma bai ce suwa ne waɗanda matakin zai shafa ba ko kuma inda za a kai su.

“Wannan mataki ne na wucen gadi a yunƙurin sake nazari kan haɗin gwiwar tsaro da za a ci gaba da yinta bayan zaɓen shugaban ƙasar Chadi na ranar 6 ga watan Mayu.” kamar yadda ya bayyana.

Sanarwar ta zo ne bayan da shugaban hafsan sojin saman Chadi, a farkon watan nan, ya umarci Amurka ta dakatar da ayyukanta a sansanin sojin sama da ke N’Djamena, babban birnin Chadi, in ji kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Gen Ryder ya kuma ce an soma tattaunawa da sojojin da ke mulki a Nijar da majalisar tabbatar da tsaron ƙasa CNSP ranar Laraba domin tabbatar da janye sojojin Amurka daga ƙasar cikin lumana.

Amurka ta dogara kan Nijar a matsayin babbar sansaninta ta bibiyar ayyukan ƴan ta’adda a yankin Sahel.

Sai dai sojojin Nijar da ke mulkin ƙasar tun Yuli, sun kawo ƙarshen yarjejeniyar tsaro da ƙasar tare da korar sojojin Faransa, wani yunƙuri na yanke alaƙa da ƙasashen yamma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp