Home Labarai Gwamnatin Tinubu tayi karin Albashi ga ma’aikatan Nijeriya

Gwamnatin Tinubu tayi karin Albashi ga ma’aikatan Nijeriya

Gwamnatin tarayya a Najeriya ta yi wa ma’aikatanta ƙarin albashi da kimanin kashi 25 cikin ɗari zuwa kashi 35 cikin ɗari.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin bukin ranar ma’aikata ta duniya.

A ranar Talata ne wata takarda daga shugaban hukumar kula da albashi ta Najeriya, Ekpo Nta ta tabbatar da ƙarin albashin.

Takardar ta nuna cewa ƙarin albashin zai fara ne daga ranar ɗaya ga watan Janairun 2024.

Kamar akasarin al’umma ƙasar, ma’aikatan gwamnati a Najeriya sun faɗa cikin mawuyacin hali sanadiyyar matsin tattalin arziƙi.

Kayan masarufi sun yi tashin gwauron zabi sannan darajar naira ta zube idan aka kwatanta da dalar Amurka duk kuwa da sabbin matakan da gwamnatin ƙasar ke ci gaba da ɗauka.

Yanzu haka akwai wani kwamiti da gwamnatin ƙasar ta kafa wanda ke aiki tare da ƙungiyoyin ƙwadago na ƙasar domin samar da matsaya kan ƙarancin albashi ga ma’aikata a ƙasar.

A baya ƙungiyoyin ƙwadago sun sha yin barazanar shiga yajin aiki da durƙusar da lamurra a ƙasar domin tursasa wa gwamnatin tarayya ɗaukan matakan bunƙasa walwalar ma’aikata.

A halin yanzu mafi ƙarncin albashin ma’aikata a hukumance shi ne naira 30,000.

Kuma duk da haka akasarin gwamnatocin jihohi ba su iya biyan ma’aikatansu albashin mafi ƙaranci, inda akan samu wasu ma’aikata na bin bashin albashin watanni da dama.

Wannan sabon albashin da gwamnatin ta amince da shi zai shafi ma’aikatan gwamnati da ke bisa tsarin CONPSS, da na ma’aikatan kwalejojin bincike na CONRAISS, da jami’an ƴansanda (CONPOSS) da ma’aikatan tattara bayanan sirri (CONICCS) da sauran masu ɗamara (CONPASS) da kuma dakarun ƙasar (CONAFSS).

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp