Home DUNIYA Atiku ya gargadi Tinubu kan tauye hakkin ‘yan Jaridu a Nijeriya

Atiku ya gargadi Tinubu kan tauye hakkin ‘yan Jaridu a Nijeriya

Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP a zaben shekara ta 2023 da ta gabata, Alhaji Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da yunkurin gwamnatin jam’iyyar APC mai mulkin  karkashin jagorancin Bola Tinubu, na murkushe yancin yada labarai da kafafen yada labarai ke da shi kundin tsarin mulki kasa na 1999 da aka yiwa gyaran fuska.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Alhaji Atiku Abubakar ya fitar kuma aka raba ga manema labarai. inda tace da ayyana yunkurin gwamnatin matsayin wata barazana ga harkokin yada labarai.

 

“Ba karamar barazana ba ce ga tabbatar da dimokaradiyyar Nijeriya, wadda ta ke damfare akan durakun bangarori guda hudu na zartarwa, dokoki, Shari’a da na yan jarida wadanda hakkin sanar da al’umma halin da kasa ta ke ciki ya rataya a wutansu”.

 

Atiku Ya yi kira ga yan jarida a kasar da cewa kada su bari wannan barazanar ta tsorata su, ta yadda zasu kasa sanar da al’umma rawar da gwamnatin da ke mulkinsu ke takawa wajen tasarrafi da al’amuran da suka shafi rayuwar su da walwalar su.

Idan za’a iya tunawa gwamnatin tarayyar Nijeriya na shan suka tun bayan da jaridar Daily Trust ta wallafa labarin kan batun yarjejeniyar Samoa da gwamantin Nijeriya, wadda ake zargin cewa akwai batun auren jinsi a cikin ta.

Lamarin da yasa gwamnatin tarayyar ta musanta, har ma ya ti barazanar daukar matakin Shari’a kan Kamfanin jaridar Daily Trust.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp