Home DUNIYA Ku daina bayyana kan ku matsayin sarakai – Umarnin Kotu ga ...

Ku daina bayyana kan ku matsayin sarakai – Umarnin Kotu ga Tsofaffin Sarakunan Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karƙashin jagorancin mai shari’a Amina Adamu, ta tabbatar da ingancin  dokar da majalisar jihar Kano ta samar wadda ta rushe sarakuna biyar da aka samar a cikin tsohowar doka.

Kotun ta ayyana cewar dokar masarautu ta shekarar 2024, wadda majalisar dokokin kano ta samar a matsayin dai-dai.

Da take yanke hukuncin a zaman ta na yau, kotun ta kuma bayyana cewar aikin majalisar dokoki shine ta yi doka, ko ta rushe doka, ko kuma ta yiwa doka gyaran fuska.

Mai shari’a Amina Adamu, ta kuma bayyana cewar Sarakunan Kano waɗanda gwamnati ta cire kada su kara kiran kansu a matsayin sarakuna, kuma su dawo da dukkanin wata kadara mallakin gwamnati wadda take hannunsu.

 

Har ila yau, kotun ta ayyana cewar jibge jami’an tsaro a gidan sarki na Nassarawa da akayi ya saɓawa doka.

 

Tun da fari gwamnatin jihar Kano ce ta shigar da ƙarar inda ta roki kotun da ta tabbatar da dokar majalisa ta 2024.

Majalisar dokokin Kano dai ta yi wa dokar masarautu gyaran fuska wanda hakan ya dawo da masarauta guda ɗaya a jahar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp