Home DUNIYA Ku daina bayyana kan ku matsayin sarakai – Umarnin Kotu ga ...

Ku daina bayyana kan ku matsayin sarakai – Umarnin Kotu ga Tsofaffin Sarakunan Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Babbar kotun jaha mai lamba 7 karƙashin jagorancin mai shari’a Amina Adamu, ta tabbatar da ingancin  dokar da majalisar jihar Kano ta samar wadda ta rushe sarakuna biyar da aka samar a cikin tsohowar doka.

Kotun ta ayyana cewar dokar masarautu ta shekarar 2024, wadda majalisar dokokin kano ta samar a matsayin dai-dai.

Da take yanke hukuncin a zaman ta na yau, kotun ta kuma bayyana cewar aikin majalisar dokoki shine ta yi doka, ko ta rushe doka, ko kuma ta yiwa doka gyaran fuska.

Mai shari’a Amina Adamu, ta kuma bayyana cewar Sarakunan Kano waɗanda gwamnati ta cire kada su kara kiran kansu a matsayin sarakuna, kuma su dawo da dukkanin wata kadara mallakin gwamnati wadda take hannunsu.

 

Har ila yau, kotun ta ayyana cewar jibge jami’an tsaro a gidan sarki na Nassarawa da akayi ya saɓawa doka.

 

Tun da fari gwamnatin jihar Kano ce ta shigar da ƙarar inda ta roki kotun da ta tabbatar da dokar majalisa ta 2024.

Majalisar dokokin Kano dai ta yi wa dokar masarautu gyaran fuska wanda hakan ya dawo da masarauta guda ɗaya a jahar Kano.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp