Home DUNIYA UAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya

UAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta dage haramcin shiga ƙasarta da ta yi wa ‘yan Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar wacce PRNigeria Hausa ta samu mai dauke da sa hannun Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai na Kasa, Mohammed Idris, a ranar Litinin.

Sanarwar ta ce bayan wata tattaunawa da gwamantin Nijeriyar ta yi da ta ƙasar, an sami cim ma matsaya da yarjejeniyar barin ‘yan Nijeriya su ci gaba da shiga kasar ta UAE.

Kazalika, sanarwar ta ce daga yarjejeniyar har da ɗage haramcin bayar da izinin shiga UAE ga dukkan ’yan Nijieriyar dake son shiga kasa

Sanarwar ta ce za a iya fara neman bizar daga 15 ga watan na Yuli, ta kuma bukaci ‘yan kasar su yi nazari kan bizar ta hanyar ziyartar shafinta na intanet domin karin bayani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp