Home Labarai Majalisar Dokokin Najeriya za ta Katse Hutunta Don Tattauna Muhimman Batutuwan ƙasar

Majalisar Dokokin Najeriya za ta Katse Hutunta Don Tattauna Muhimman Batutuwan ƙasar

Majalisar wakilan Najeriya za ta katse hutunta na shekara domin yin wani zama a ranar Laraba da nufin tattauna muhimman batutuwan da suka buƙaci majalisar ta yi magana a kan su.

Bayanin hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa daga magatakarda na majalisar Yahaya Danzaria.

Taron zai ƙunshi tattaunawa da matasa ƴan Najeriya a wani taro da kakakin majalisar Tajuddeen Abbas zai karɓi baƙunci.

Taron zai haɗa da shugabannin matasa da ɗalibai daga manyan makarantu da ƙwararru matasa da kuma wakilai daga ƙungiyoyin matasa da ƙungiyoyin farar hula.

An tsara taron domin bai wa matasa ƴan Najeriya damar bayyana damuwarsu su kuma bayyana ra’ayoyinsu sannan su tattauna da jagororin majalisa kan matsalolin da suka shafi rayuwarsu da kuma gobensu.

Majalisar wakilan ta soma hutu ne ranar Talatar da ta gabata inda ta shirya dawowa ranar 17 ga watan Satumba.

Shi ma shugaban majalisar dattijai, Sanata Godswill kpabio ya kira taron gaggawa don tattauna al’amuran ƙasar, kamar yadda sanarwa daga magatakardan majalisar, Chinedu Akubueze ta bayyana.

Sai dai sanarwar ba ta yi cikakken bayani ba game da abin da taron zai mayar da hankali a kai.

Za a yi taron ranar Laraba, 31 ga watan Yuli, kwana ɗaya kafin gagarumar zanga-zangar da aka shirya yi a faɗin Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp