Home Labarai Mayakan boko haram 50 sun mika wuya ga Sojoji a jihar Borno

Mayakan boko haram 50 sun mika wuya ga Sojoji a jihar Borno

Nigerian Army

Dakarun sojojin kasan Nijeriya sun sami nasarar kama kwamandan kungiyar Boko, mai kai musu kaya da kuma wadanda suke hada baki, gami da mayakan kungiyar da suka mika wuya da iyalansu.

Haka kuma dakarun rundunar sun sami nasarar kwato wadanda mayakan kungiyar suka yi garkuwa da su a mabambanta maboyar su, haka kuma dakarun sun sami nasarar kwato wasu kayyaki da bata gari suka sace a yayin gudanar da zanga-zangar luma a kasar.

Rundunar sojojin tace a ranar 4 ga watan Agusta, 2024 bisa aiki da wasu bayanan sirri dake yi ta sami nasarar kama wasu kwamandojin mayakan kungiyar boko haram a jihar Borno, wadanda ke yunkurin kutsawa sansanin ‘yan gudun hijira dake Damasak a karamar hukumar Mobbar.

Wadanda ake zargin da suka hadar da Bana Yamode da babagana Usman, wanda suka yi ikirarin sun je sansanin ne domin ziyartar iyalen su, wadanda tun da fari dama su sukayi jagoranci kai hari a yankin.

Haka kuma dakarun sun sami nasara kama wadanda ake zargi da safarar kayayyaki guda biyu Mallam Mustapha Isma’il mai shekaru 49 da kuma Abdulmudalibi Haruna mai shekaru 30, tare da ceto wasu mutum biyu a yayin sumamen.

Haka kuma mayakan boko haram 50 da iyalansu sun mika wuya ga rundunar a kananan hukumomin Bama, Gwoza da Dikwa, wannan dai na zuwa ne bisa yunkurin dakarun sojojin na kakkabe mayakan na boko haram.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp