Home Labarai NBS- Jihar Kano ta rabauta da sama da biliyan biyun don inganta...

NBS- Jihar Kano ta rabauta da sama da biliyan biyun don inganta muhalli

Jihar Kano ta karbi kaso mai tsoka daga kwamitin rabon arzikin kasa, wanda hakan ya sanya jihar zama kan gaba cikin jihohin kasar 36, a tsakanin watan yunin shekarar 2023, zuwa watan yunin wannan shekara.

Hukumar kididdiga ta kasa NBS ce ta fitar da rahoton dake nuna cewa jihar Kano a tsakanin lokacin ta rabauta da kudi naira Biliyan 2 da milyan daya, domin amfani da kudin wajen magance matsalolin da suka shafi muhalli a jihar.

Daga cikin manufar bayar da kudin gwamnatin tarayya na fatan jihohin kasar suyi amfani da kudin, wajen magance matsalolin muhalli irin su kwararowar hamada, ambaliyar ruwa, da kuma zaizayar kasa.

A yan shekarun da suka gabata, gwamnatin tarayya ta baiwa jihohi naira Biliyan 38.62, wanda kuma jihar Kano ta zama kan gaba wajen karba naira miliyan 175 duk wata domin gudanar da wadancan ayyuka.

Rahoton yace Jihar Borno dake fama da matsalar masu tayar da kaya baya na boko haram da yadda muhalli ya salwanta a wannan jiha, bata kai Kano karbar kaso mai tsoka ba, domin kuwa Borno duk wat ana rabauta da naira Milyan 140 ne kaca, wato Kano ta bata tazarar naira miliyan 35 ke nan a yadda rahoton hukumar NBS ya bayyana.

Sassa da dama yanzu haka na jihar nan na fama da matsalar zaizayar kasa, musamman garin daba dake yankin karamar hukumar Dawakin Kudu, zaizayar kasar dake ci gabar da haifar da koma baya ga manoman yankin kuma a kullum kira suke ga gwamnati amma a cewarsu har yanzu shiru.

Shi dai wannan kudi akan ware kaso 2 cikin dari na arzikin kasa, tare da baiwa ofishin kula da asusun taimakawa muhallin wanda ke karkashin ofishin sakataren gwamnatin tarayya, kuma tun a shekarar 1981 aka fara wannan tsari.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp