Home Labarai NBS- Jihar Kano ta rabauta da sama da biliyan biyun don inganta...

NBS- Jihar Kano ta rabauta da sama da biliyan biyun don inganta muhalli

Jihar Kano ta karbi kaso mai tsoka daga kwamitin rabon arzikin kasa, wanda hakan ya sanya jihar zama kan gaba cikin jihohin kasar 36, a tsakanin watan yunin shekarar 2023, zuwa watan yunin wannan shekara.

Hukumar kididdiga ta kasa NBS ce ta fitar da rahoton dake nuna cewa jihar Kano a tsakanin lokacin ta rabauta da kudi naira Biliyan 2 da milyan daya, domin amfani da kudin wajen magance matsalolin da suka shafi muhalli a jihar.

Daga cikin manufar bayar da kudin gwamnatin tarayya na fatan jihohin kasar suyi amfani da kudin, wajen magance matsalolin muhalli irin su kwararowar hamada, ambaliyar ruwa, da kuma zaizayar kasa.

A yan shekarun da suka gabata, gwamnatin tarayya ta baiwa jihohi naira Biliyan 38.62, wanda kuma jihar Kano ta zama kan gaba wajen karba naira miliyan 175 duk wata domin gudanar da wadancan ayyuka.

Rahoton yace Jihar Borno dake fama da matsalar masu tayar da kaya baya na boko haram da yadda muhalli ya salwanta a wannan jiha, bata kai Kano karbar kaso mai tsoka ba, domin kuwa Borno duk wat ana rabauta da naira Milyan 140 ne kaca, wato Kano ta bata tazarar naira miliyan 35 ke nan a yadda rahoton hukumar NBS ya bayyana.

Sassa da dama yanzu haka na jihar nan na fama da matsalar zaizayar kasa, musamman garin daba dake yankin karamar hukumar Dawakin Kudu, zaizayar kasar dake ci gabar da haifar da koma baya ga manoman yankin kuma a kullum kira suke ga gwamnati amma a cewarsu har yanzu shiru.

Shi dai wannan kudi akan ware kaso 2 cikin dari na arzikin kasa, tare da baiwa ofishin kula da asusun taimakawa muhallin wanda ke karkashin ofishin sakataren gwamnatin tarayya, kuma tun a shekarar 1981 aka fara wannan tsari.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp