Home Labarai Gwamnan Kano ya bayar da umarnin bincikar badakar sayen magunguna a jihar

Gwamnan Kano ya bayar da umarnin bincikar badakar sayen magunguna a jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa bashi da masaniya kan kwangilar samar da magunguna a kananan hukumomi 44 na jihar.

wannan na cikin wata Sanarwar da kwamishinan yada Labarai na jihar Baba Halilu Dan Tiye ya fitar wadda aka rabawa manema labarai, ta ce Gwamnan Abba ya umurci Shugaban Hukumar karbar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano da ta gaggauta bincikar wannan zargi tare da bayar da rahoton sakamakon da ya dace domin daukar matakin da ya dace.

Sanarwar ta ci gaba da cewa manufar binciken shine bankado gaskiyar Lamarin domin tabbar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da shugabanci na gari ga alummar Kano baki daya.

Daga bisani Gwamna Yusuf ya kuma bukaci daukacin al’ummar Kano da su yi hakuri har a kammala bincike.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp