Home General Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban ƙungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, bisa rakiyar ƴan ƙungiyar ƙwadago da Femi Falana, lauyoyi da suka haɗ da Femi Falana lauya mai rajin kare hakkin ɗanadam a Najeriya da Deji Adeyanju, ya gana da ƴansanda a hedikwatarsu da ke babban birnin tarayya domin amsa gayyatar suka yi masa.

Rundunar ‘yan sandan dai ta gayyaci shugaban NLC ɗin ne bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta’addanci, wanda shugaban da ƙungiyar suka musanta.

Tun da karfe takwas na safe ne shugabannin NLC ɗin suka fara hallara a hedikwatarsu, inda suka gudanar da gangamin nuna hadin kai da goyon baya ga Ajaero.

Bidiyon da aka wallafa a shafin sada zumuntar NLC na X sun nuna wasu shugabannin kwadagon suna jawabi ga ma’aikatan da suka taru, wadanda suka tsaya kyam a bayan Shugaban nasu.

Kawo yanzu dai babu cikakken bayani na haƙiƙanin abin da ya faru a yayin ganawar.

Tun da farko dai ‘yan sandan sun gayyaci Ajaero a makon da ya gabata, bisa zargin bayar da kudade ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan sada zumunta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp