Home General Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna tace sojoji sun hallaka ‘yan bindiga takwas a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar alhamis.

Yace sakamakon wani sumame da dakarun sojin suka kai yankin Kamfanin Doka, ne suka yi arba da ‘yan bindigar a yankin, nan suka hau musayar wuta ne sojojin suka sami nasarar hallaka bakwai daga cikin su.

“Ya yin da sojojin ke bincike a yankin sun sami nasarar bankado bindiga kirar AK47 guda uku, gami da gidan saka alburushi guda takwas, wanda suka kunshi hudu babu komai a cikin su sai kuma hudu dauke da alburusai 120 masu tsahon 7.62mm.” a cewar sa.

Aruwan ya kara da cewa sun kuma sami nasarar kwato kayayyakin da suka hadar da babu 6, wayoyin hannun uku, sai kuma radio kirar Baofeng, da kuma kayan fararen hula.

Haka kuma ya kara da cewa yayin da sojojin ke karkare atisayen sun sake yin wata arangamar da ‘yan ta’addan a yankin Gayam.

“Sojojin sun sami nasarar hallaka daya daga cikin su yayin da ake zargin sauran sun gudu da raunikan harbi a jikin su.” Kamar yadda ya bayyan.

Aruwana ya kara da cewa Gwamnan jihar Uba Sani ya yaba da kokarin dakarun bisa wannan nasara da suka samu a yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi sassan jihar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp