Home General Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Sojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna tace sojoji sun hallaka ‘yan bindiga takwas a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gidan Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar alhamis.

Yace sakamakon wani sumame da dakarun sojin suka kai yankin Kamfanin Doka, ne suka yi arba da ‘yan bindigar a yankin, nan suka hau musayar wuta ne sojojin suka sami nasarar hallaka bakwai daga cikin su.

“Ya yin da sojojin ke bincike a yankin sun sami nasarar bankado bindiga kirar AK47 guda uku, gami da gidan saka alburushi guda takwas, wanda suka kunshi hudu babu komai a cikin su sai kuma hudu dauke da alburusai 120 masu tsahon 7.62mm.” a cewar sa.

Aruwan ya kara da cewa sun kuma sami nasarar kwato kayayyakin da suka hadar da babu 6, wayoyin hannun uku, sai kuma radio kirar Baofeng, da kuma kayan fararen hula.

Haka kuma ya kara da cewa yayin da sojojin ke karkare atisayen sun sake yin wata arangamar da ‘yan ta’addan a yankin Gayam.

“Sojojin sun sami nasarar hallaka daya daga cikin su yayin da ake zargin sauran sun gudu da raunikan harbi a jikin su.” Kamar yadda ya bayyan.

Aruwana ya kara da cewa Gwamnan jihar Uba Sani ya yaba da kokarin dakarun bisa wannan nasara da suka samu a yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi sassan jihar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp