Home DUNIYA Jami’an NEMA sun fara kai agaji Maiduguri

Jami’an NEMA sun fara kai agaji Maiduguri

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta ce ta fara kai agaji domin kwashe mutanen da ambaliyar ruwa ta ɗaiɗaita a Maiduguri, babban birnin jihar Borno; ambaliyar ta biyo bayan fashwar madatsar ruwa.

Wannan dai na cikin wata sanawar da babbar darektar hukumar Zubaida Umar ta fitar a shafinta na X, ta ce sun kuma fara shirye-shiryen tallafa wa mutanen da lamarin ya shafa da abinci, matsuguni da kuma magaunguna.

Yankunan da ambaliyar ta shafa sun haɗa da Shehuri, rukunin gidaje da ke G.R.A, Gambomi, Budum, Bulabulin, Adamkolo, Millionaires Quarters, kasuwar Monday Market da kuma Gwange.

NEMA ta ce gwamnatin jihar Borno ta buɗe sansanin Bakassi domin tsugunar da mutanen da ambaliyar ta shafa.

Ta ce suna aiki da hukumar ba da agaji reshen jihar ta Borno domin tallafa wa mutanen da ke cikin sansanin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp