Home General Tinubu ya taya al’ummar Maiduguri jimami kan iftila’in ambaliya

Tinubu ya taya al’ummar Maiduguri jimami kan iftila’in ambaliya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya nuna matukar damuwarsa game da ambaliyar ruwa da ta afku a wasu sassan Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar.

Ambaliyar ruwan ita ce mafi muni a cikin shekarun baya-bayan nan da birnin ya fuskanta yayin da ta raba dubban mutane da muhallansu tare da yin ɓarna a karamar ofishin gidan waya da asibitin koyarwa na Maiduguri.

Tinubu ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar, musamman waɗanda suka yi asara sakamakon bala’in da ambaliyar ruwan ta haddasa.

Tinubu ya kuma yi kira da a gaggauta kwashe mutane daga yankunan da abin ya shafa yayin da hukumomi ke ci gaba da tantance irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

Shugaban ya kuma umurci hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) da ta taimaka wa waɗanda ambaliyar ta shafa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp