Home Labarai Shugabanni ba su da rigar kariya a Musulunci – Pantami

Shugabanni ba su da rigar kariya a Musulunci – Pantami

Kashifu pantami

Tsohon ministan sadarwa a Najeriya, farfesa Isa Ali Pantami ya yi kira da a yi watsi da tsarin ba shugabanni rigar kariya.

Pantami ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Abuja a wajen taron shekara-shekara na cibiyar Musulmi wato the Muslim Congress (TMC) mai taken; ‘Gina ingantacciyar ƙasa: Nauyi ne kan shugabanni da mabiya domin tuna ranar ƴancin Najeriya na 64.

“A Musulunci, babu wata rigar kariya domin kariyar za ta ba mutum wata dama ce kawai a lokacin da yake shugabanci, wanda ba za ka samu ba, bayan ka bar ofis. Wasu lokutan kariyar na da kyau, amma a wasu lokutan hakan na jawo maka matsaloli da yawa ne,” in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ya ƙara da cewa, “da zarar ka bar ofis bayan shekara huɗu ko takwas sai ka ga ana ƙalubalantakarka da tuhume-tuhume da dama, wasu har guda 120 ma. Don haka kariyar ba ta hana mutum fuskantar shari’a, kawai tana jawo kawo jinkiri ne da kuma ba mutum damar ƙara aikata wasu laifukan.

“A shari’ar Musulunci babu wata rigar kariya. Da shugaba da mabiya kowa zai iya fuskantar shari’a, kuma dole ya je ya kare kansa. An yi wa Ali ibn Abi Talib da Umar ibn Khatab suna Khalifanci. Don haka yana da kyau a samar da daidaito a wajen shari’a,” in ji Pantami.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp