Home Labarai ‘Dole Najeriya ta ci gaba da gyaran tattalin arziki da take yi...

‘Dole Najeriya ta ci gaba da gyaran tattalin arziki da take yi tsawon shekara 15’

Bola Ahned Tinubu

Bankin Duniya ya ce dole ne Najeriya ta ci gaba da yin tsare-tsaren da take kai a yanzu na tsawon aƙalla shekara 15, muddin tana son ɗorewar tattalin arzikinta.

Mataimaikin shugaban bankin, Mr Indermit Gill ne ya bayyana haka a wani taron tattalin arziki karo na 30 da aka yi a Abuja ranar Litinin.

Ya ce ya kamata gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da tsare-tsarenta na yanzu domin shawo kan matsaloli da ƙasar ke fuskanta wanda kuma suka janyo rashin cigaba tsawon lokaci.

“Babu wani wayo da za a yi a batun gyaran tattalin arziki. Ya kamata Najeriya ta tsaya kan tsare-tsarenta na tsawon shekara 15. Tsare-tsaren da aka ɗauka yanzu ba za su yi daɗi ba ko kuma kawo sakamako mai kyau nan take, amma za su ɗora ƙasar kan turbar cigaba mai ɗorewa,” in ji shi.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin ƴan Najeriya ke ci gaba da nuna fushinsu kan cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi da kuma tashin farashin dala.

Duk da cewa waɗannan tsare-tsare sun janyo tsadar rayuwa da kuma wahalhalu daban-daban ga ƴan ƙasar, jami’in na Bankin Duniya ya ce komawa baya ba zai haifar da ɗa mai ido ga tattalin arzikin ƙasar ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp