Home General Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Kungiyar likitoci ta baiwa gwamnan Kano awanni 48 ya kori Kwamishiniyar sa

Ƙungiyar Likitoci, NMA, reshen jihar Kano ta baiwa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar wa’adin awanni 48 da ya kori Kwamishiniyar Jin-ƙai da Walwalar Al’umma, Amina Abdullahi bisa zargin cin zarafin wata likita to ta tafi yakin aiki.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar, Dr Abdulrahman Ali da sakataren sa, Dr. Ibrahim D. Muhammad su ka fitar ta ce lamarin ya faru ne a ɓangaren yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad lokacin da likitar take duba marasa lafiya.

A cewar NMA, Kwamishiniyar ta je asibitin ne tare da tawogar ta, inda ta ci zarafin likitar saboda ta ce mata babu magungunan da Kwamishiniyar ta tambaya.

NMA ta kara da cewa a lokacin da lamarin ta faru, likitar ita kaɗai ce ke duba marasa lafiya sama da 100, “amma aka ci zarafin ta saboda wani abu da bata da iko a kai.”

“Hakan ya nuna yadda masu rike da mukamin siyasa ke ba zarar da ofishin su kuma ya nuna irin matsalar da ake da ita a fannin lafiya.

“Saboda haka mun bakwa gwamnan Kano awanni 48 da ya sallami Kwamishiniyar. In ba haka ba, to lamarin ba zai haifar da ɗa mai ido ba domin za mu janye aiyukan mu,”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp