Home General Likitocin Kano sun janye yajin aiki da suka tsunduma

Likitocin Kano sun janye yajin aiki da suka tsunduma

Kungiyar Likitoci na jihar Kano sun janye yajin aikin da suka fara a daren jiya, bayan Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif ya sami nasarar sasanta rikicin dake faruwa, tsakanin kungiyar da kuma Kwamishiniyar Ma’aikatar Jin-kai ta jihar.

Shugaban Kungiyar Likitoci na jihar Kano Dakta Abdurrahman ne ya tabbatar da hakan, a yayin zantawar sa da manema Labaran a fadar Gwamnatin Kano.

Sanarwar da Kakakin Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aiko wa jaridar PRNigeria ta kara da cewa, yanzu haka Likitocin sun koma bakin aiki domin ci-gaba da bawa marasa lafiya cikakkiyar kulawar da suka saba.

Dakta Abdurrahman ya ce sun janye yajin aikin ne bayan wani zama na musamman da Gwamnan Kano, akan sabanin da aka samu a tsakanin Mambar tasu da kuma ita waccan Kwamishiniya.

Ya kuma yaba wa Gwamnan a bisa gaggawar daukar matakin da ya kamata akan lamarin, harma yayi kira ga al’ummar jihar da su dinga bin dukkan hanyoyin da suka dace wajen shigar da korafin su akan jami’an lafiya domin a sami damar yin adalci ta hanyar bincika wa dama daukar matakin da ya kamata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp