Home General Dalilin Ndume na sa alamar tambaya kan gaggawar amincewa da ƙudurin haraji...

Dalilin Ndume na sa alamar tambaya kan gaggawar amincewa da ƙudurin haraji na Tinubu

Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta kudu ya ɗiga alamar tambaya kan yadda ake gaggawa domin amincewa da ƙudurin harajin da shugaban ƙasa Tinubu ya aika majalisa.

Ndume ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da tashar Channels a shirin Politics Today.

Sanatan ya ce a zaɓen 2023, sanatoci 25 ne kawai suka dawo, wanda hakan a cewarsa ke nuna cewa mutane sun fara daina amince da su.

Ya ƙara da cewa yadda ake gaggawar amincewa da ƙudurin na harajin, ya nuna kamar akwai lauje cikin naɗi.

“Ba wai ina da matsala da ƙudurin ba ne, kuma ba wai ina cewa a yi watsi da shi ba ne baki ɗaya, amma tunda gwamnoninmu waɗanda su ne jagororinmu da kuma majalisar tattalin arziki da wasu ɗaiɗaikun mutane sun bayyana cewa akwai buƙatar ƙarin lokaci domin a tattauna, ya kamata a ɗan ƙara lokaci. Me ya sa ake gaggawa?” in ji shi.

Ndume ya ce babbar matsalarsa da ƙudurin ita ce lokacin da aka bijiro da ita, inda a cewarsa bai kamata a ce an kawo maganar ƙudurin ba a daidai wannan lokacin da ƴan Najeriya suke cikin ƙuncin rayuwa.

“Tun kakanninmu uuna biyan haraji a arewa. Don haka ba wai muna tsoron biyan haraji ba ne, duk wani ɗan ƙasa na ƙwarai zai biya haraji, amma gaskiya zuwa da wannan maganar a wannan lokacin bai dace ba,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp