Home General Saƙon Tinubu na sabuwar shekara soki-burutsu ne – PDP

Saƙon Tinubu na sabuwar shekara soki-burutsu ne – PDP

Babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP ta ce jawabin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wa al’ummar kasar na sabuwar shekara, kalaman baka ne kawai.

A jawabin da Tinubun ya yi ranar Laraba 1 ga watan Janairun, 2025, ya bayyana tsare-tsaren da ya ce gwamnatinsa za ta bullo da su domin rage tsadar farashin abinci da samar da tsaro da kuma wasu nasarori da ya ce gwamnatinsa ta samu.

Ya ce duk abubuwan da Tinubun ya fada na cewa gwamnatinsa ta samu nasara, kamata ya yi a ce an gan su a fili muraran, kamar yadda akan ce, ”an ce da kare ana biki a gidanku ya ce to mu gani a kasa.”

Tsauri ya ce duk abubuwan da ya fada ba a takarda ya kamata a gan su ba, yana mai nuni da cewa idan har gaskiya ne gwamnatin ta samu wannan nasara da Tinubun ya fada to jama’a su gani amma lamartin sabanin haka yake.

”Ba abin mamaki ba ne in Shugaban Kasa ya yi wadannan maganganu domin kawai ya sanar da ‘yan Najeriya ba don ya dadada masu ba, don duk abin da ya fadi kowa ya sani ba za a ce karya ba ne amma ba gaskiya ba ne – misali in an ce mana farashin mai ya ragu yaushe ya ragu?” In ji shi.

Ya ce gwamnati na cewa farashin dala ya ragu naira ta kara samun daraja, to amma ya yi nuni da cewa, ” mun wayi gari dala ta koma naira 1600 daga naira 1700, cewa ake an samu nasara, to wace nasara aka samu bayan lokacin da Buhari ya hau mulki muna sayen dala naira tamanin?”

”To wane irin cigaba ne wannan? Mu a wurinmu Turanci ne aka rubuta kuma ya karantu,” in ji shi.

A dangane da kalaman shugaban ne jam’iyyar PDP ta bakin tsohon sakatarenta na kasa Sanata Umaru Tsauri, ta mayar da martani da cewa kalaman soki-burutsu ne kawai.

A tattaunawarsa da BBC, Tsauri ya ce, abubuwan da shugaban ya karanta abin da su suka dauka an rubuta masa Turanci ne kawai ya karanta, amma ba wai abubuwa ne da suke a zahirin gaskiya ba.

Ya ce duk abubuwan da Tinubun ya fada na cewa gwamnatinsa ta samu nasara, kamata ya yi a ce an gan su a fili muraran, kamar yadda akan ce, ”an ce da kare ana biki a gidanku ya ce to mu gani a kasa.”

Tsauri ya ce duk abubuwan da ya fada ba a takarda ya kamata a gan su ba, yana mai nuni da cewa idan har gaskiya ne gwamnatin ta samu wannan nasara da Tinubun ya fada to jama’a su gani amma lamartin sabanin haka yake.

”Ba abin mamaki ba ne in Shugaban Kasa ya yi wadannan maganganu domin kawai ya sanar da ‘yan Najeriya ba don ya dadada masu ba, don duk abin da ya fadi kowa ya sani ba za a ce karya ba ne amma ba gaskiya ba ne – misali in an ce mana farashin mai ya ragu yaushe ya ragu?” In ji shi.

Ya ce gwamnati na cewa farashin dala ya ragu naira ta kara samun daraja, to amma ya yi nuni da cewa, ” mun wayi gari dala ta koma naira 1600 daga naira 1700, cewa ake an samu nasara, to wace nasara aka samu bayan lokacin da Buhari ya hau mulki muna sayen dala naira tamanin?”

”To wane irin cigaba ne wannan? Mu a wurinmu Turanci ne aka rubuta kuma ya karantu,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp