Home General Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air

Gwamnatin Nijeriya ta dakatar da Jirgi Max Air

Gwamnatin Najeriya ta hannun Hukumar kula da sufurin jragen sama ta ƙasar (NCAA) ta sanar da dakatar da ayyukan kamfanin jirgin sama na Max Air, bayan jirgin kamfanin ya yi hatsari a daren jiya Talata a jihar Kano.

Daraktan hulɗa da jama’a da kare haƙƙin abokan hulɗa na hukumar, Michael Achimugu – wanda ya fitar da sanarwar – ya ce dakatarwar za ta soma aiki ne a daren 31 ga watan Janairun 2025, domin bai wa hukumomin kamfanin damar tattance ayyukanta a cikin gida da ya haɗa da bincike kan kamfanin, ma’aikatansa, tsarin aikinsa da jiragensa, da kuma tattalin arziƙin kamfanin.

Achimugu ya kuma ce tuni hukumar tabbatar da kariya (NSIB) ta ƙaddamar da bincike kan musabbabin haɗarin na baya-bayan nan.

Jirgin Max Air samfurin B734 mai lambar rijista 5N-MBD, ya yi haɗari ne a yayin sauka a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano da ke Kano bayan tayarsa ta fashe a jiya Talata.

Duk da dai fasinjoji 53 da ke cikin jirgin sun fita lafiya, hukumar kula da filayen jiragen sama ta ƙasar (FAAN) ta rufe filin jirgin na wucin-gadi kafin buɗe shi a safiyar ranar Laraba.

Wannan ne karo na uku da ake samun haɗarin jirgin na Max Air a cikin wata uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp