Home General Majalisar dinkin Duniya ta zargi RSF da haifar da tarnaƙi a Sudan

Majalisar dinkin Duniya ta zargi RSF da haifar da tarnaƙi a Sudan

Majalisar Ɗinkin Duniya ta zargi mayaƙan rundunar RSF, da hana isar da kayan agaji yankin Darfur da ke fuskantar barazanar yunwa a Sudan da yaƙi ya ɗai-ɗaita.

A cikin wata sanarwa da jami’ar kula da ayyukan jin kai, ta Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Sudan Clementine Nkweta-Salami ta fitar, ta ce wasu dokoki da RSF ta sanya a yankin na Darfur, na haifar da tarnaƙi wajen gudanar da ayyukan ceton rayukan jama’a.

Dakarun na RSF da ke fafata yaƙi da sojojin Sudan tun a watan Afrelun shekarar 2023, sun kasance masu rike da ikon yankin na Darfur, musammann yadda su ka mamaye birnin El-Fasher da ke Arewacinsa a watan Mayun shekarar da ta gabata.

An dai ayyana ɓarkewar yunwa a wasu yankuna biyar na Arewacin Darfur, kuma ana zaton ta ƙara bazuwa zuwa wasu yankuna biyar nan da watan Mayu mai zuwa.

A cewar wasu alkaluma da wata ƙungiya da ke samun goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, sun nuna cewa kimanin mutum miliyan 7 ne ke fuskantar yunwa a yankin na Darfur.

A cewar wasu alkaluma da wata ƙungiya da ke samun goyon bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, sun nuna cewa kimanin mutum miliyan 7 ne ke fuskantar yunwa a yankin Darfur.

Majalisar Ɗinkin Duniya dai ta buƙaci RSF ta sauƙaƙa dokokin da ta sanya a yankin, don bada damar isar da kayan agaji ga al’ummar da ke cikin tsananin buƙata.

Shi dai yaƙin na Sudan ya lakume rayukan ɗaruruwan mutane, ya kuma raba sama da mutum miliyan 12 da muhallansu, sannan akwai wasu kimanin miliyan 25 da ke fuskantar barazanar yunwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp