Home General Najeriya da Nijar da kuma Aljeriya sun cimma yarjejeniyar shimfiɗa bututun gas...

Najeriya da Nijar da kuma Aljeriya sun cimma yarjejeniyar shimfiɗa bututun gas zuwa Turai

Ƙasashen Aljeriya da Najeriya da kuma Jamhuriyar Nijar, sun ƙulla sabuwar yarjejeniya da nufin gaggauta gudanar da akin shimfiɗa bututun iskar gas mai tsawon kilomita sama da dubu 4, da zai sada ƙasashen da nahiyar Turai.

A yarjejeniyar, ƙasashen 3 sun amince su yi amfani da bututun Transmed wanda Aljeriya ke amfani da shi don bai wa Italiya makamashin gas, sai a yanzu maimakon Italiya kawai da ke cin gajiyarsa, za a riƙa tura makamashin zuwa sauran ƙasashen Turai.

Yarjejeniyar da wakilan ƙasashen uku suka rattaba wa hannu ranar Talata da ta gabata, ta fayyace adadin kuɗaɗe da tsawon lokacin da ake buƙata don aiwatar da wannan aikin, sai kuma batun biyan diyya da kuma zaɓen ƙmfanonin da za su aiwatar da wannan aiki.

Tun a shekara ta 2009 ne ƙasashen 3 suka tattaunawa domin shimfiɗa wannan bututu mai tsawo kilomita dubu 4 da 128, kuma tun a wancan lokaci an kiyasta cewa ana bukatar Dala bilyan 10 domin aiwatar da aikin.

Rikicin Rasha da Ukraine ne ya ƙara zaburar da waɗannan ƙasashe domin gaggauta aiwatar da wannan aiki na bututun iskar gas, musamman lura da cewa tun a 2022 mafi yawan ƙasashen Turai sun bayyana aniyarsu ta daina dogara da Rasha domin samun makamashin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp