Home General Ƙasashen AES sun yi wa jakadunsu a Aljeriya ƙiranye

Ƙasashen AES sun yi wa jakadunsu a Aljeriya ƙiranye

Ƙasashen kungiyar  AES sun yi wa jakadunsu da ke Aljeriya kiranye a jiya lahadi ,bayan Mali ta zargi kasar da ƙaƙƙabo wani jirgin yakinta mara matuki a kusa da Tinzaouatene.

A cikin  daren 31 ga watan Maris da ya gabata wayewa safiyar 1 ga watan nan na Afrilu Aljeriya ta sanar da ƙaƙƙabo wani jirgi mara matuki mallakin sojojin Mali da ta zarga da keta sararin samaniyarta a kusa da Tinzaouatene da ke kan iyakar kasashen biyu.

A wata sanarwa da suka fitar a jiya lahadi kasashen AES wato Mali,Nijar da Burkina Faso sun bayyana bakin cikinsu da afkuwa lamarin tareda jaddada cewa kai hari kan daya daga cikin kasashen tamkar kaiwa baki dayan kungiyar hari ne.

Ministan harakokin wajen Mali Abdoulaye Diop ya bayyana lamarin da mai matukar muni ,lura da yadda tarwatsa jirgin ya hana dakarun kasar  cimma burinsu na ƙaƙƙabe wani gungun ‘yan ta’adda da ke tsara kai hare-hare kan kasashen AES.

Ƙasashen na  AES wato Mali da Nijar da kuma Burkina Faso sun zargi Aljeriya da taƙalar fada sanan sun sha alwashin kai kararta a gaban hukumomin ƙasa da ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp