Home General Ƙasashen AES sun yi wa jakadunsu a Aljeriya ƙiranye

Ƙasashen AES sun yi wa jakadunsu a Aljeriya ƙiranye

Ƙasashen kungiyar  AES sun yi wa jakadunsu da ke Aljeriya kiranye a jiya lahadi ,bayan Mali ta zargi kasar da ƙaƙƙabo wani jirgin yakinta mara matuki a kusa da Tinzaouatene.

A cikin  daren 31 ga watan Maris da ya gabata wayewa safiyar 1 ga watan nan na Afrilu Aljeriya ta sanar da ƙaƙƙabo wani jirgi mara matuki mallakin sojojin Mali da ta zarga da keta sararin samaniyarta a kusa da Tinzaouatene da ke kan iyakar kasashen biyu.

A wata sanarwa da suka fitar a jiya lahadi kasashen AES wato Mali,Nijar da Burkina Faso sun bayyana bakin cikinsu da afkuwa lamarin tareda jaddada cewa kai hari kan daya daga cikin kasashen tamkar kaiwa baki dayan kungiyar hari ne.

Ministan harakokin wajen Mali Abdoulaye Diop ya bayyana lamarin da mai matukar muni ,lura da yadda tarwatsa jirgin ya hana dakarun kasar  cimma burinsu na ƙaƙƙabe wani gungun ‘yan ta’adda da ke tsara kai hare-hare kan kasashen AES.

Ƙasashen na  AES wato Mali da Nijar da kuma Burkina Faso sun zargi Aljeriya da taƙalar fada sanan sun sha alwashin kai kararta a gaban hukumomin ƙasa da ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp