Home General Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojojin Najeriya a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojojin Najeriya a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun ƙaddamar da farmaki kan sansanin sojin Najeriya da ke Ƙaramar Hukumar Marte a jihar Borno, inda suka kashe wani adadi na sojojin da ba a bayyana ba.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da harin wanda aka kai da misalin karfe 3 na safiyar wannan Litinin kan sansanin sojin na Forward Operation mai ɗauke da bataliya ta 153 kamar yadda jaridar Daily Trust da ake wallafawa a Najeriyar ta rawaito.

Ɗaya daga cikin majiyoyin da ya buƙaci sakaya sunansa ya shaida wa manema labarai cewa, mayaƙan na Boko Haram sun kuma yi garkuwa da wasu sojojin na Najeriya bayan sun raba su da muhallansu a yayin farmakin.

ISWAP ta karɓe iko da Marte, sun kashe wani adadi na sojoji, sun kuma yi garkuwa da wasu, wasu da dama sun tsere zuwa Dikwa, kuma yanzu haka suna samun mafaka a sansanin runduna ta 24 da ke Dikwa

Ƴanta’addar sun kona tankunan yaƙi tare da awon gaba da tarin makamai daga sansanin sojin a cewar majiyar tsaron.

Ƙaramar Hukumar Marte dai, na da tazarar kilomita 38 daga Ƙaramar Hukumar Dikwa a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya

Wata majiya a Dikwa ta shaida wa Daily Trust cewa, an jiyo ƙarar harbe- harbe

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp