Home General Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojojin Najeriya a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojojin Najeriya a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun ƙaddamar da farmaki kan sansanin sojin Najeriya da ke Ƙaramar Hukumar Marte a jihar Borno, inda suka kashe wani adadi na sojojin da ba a bayyana ba.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da harin wanda aka kai da misalin karfe 3 na safiyar wannan Litinin kan sansanin sojin na Forward Operation mai ɗauke da bataliya ta 153 kamar yadda jaridar Daily Trust da ake wallafawa a Najeriyar ta rawaito.

Ɗaya daga cikin majiyoyin da ya buƙaci sakaya sunansa ya shaida wa manema labarai cewa, mayaƙan na Boko Haram sun kuma yi garkuwa da wasu sojojin na Najeriya bayan sun raba su da muhallansu a yayin farmakin.

ISWAP ta karɓe iko da Marte, sun kashe wani adadi na sojoji, sun kuma yi garkuwa da wasu, wasu da dama sun tsere zuwa Dikwa, kuma yanzu haka suna samun mafaka a sansanin runduna ta 24 da ke Dikwa

Ƴanta’addar sun kona tankunan yaƙi tare da awon gaba da tarin makamai daga sansanin sojin a cewar majiyar tsaron.

Ƙaramar Hukumar Marte dai, na da tazarar kilomita 38 daga Ƙaramar Hukumar Dikwa a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya

Wata majiya a Dikwa ta shaida wa Daily Trust cewa, an jiyo ƙarar harbe- harbe

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp