Home General Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojojin Najeriya a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojojin Najeriya a Borno

Mayaƙan Boko Haram sun ƙaddamar da farmaki kan sansanin sojin Najeriya da ke Ƙaramar Hukumar Marte a jihar Borno, inda suka kashe wani adadi na sojojin da ba a bayyana ba.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da harin wanda aka kai da misalin karfe 3 na safiyar wannan Litinin kan sansanin sojin na Forward Operation mai ɗauke da bataliya ta 153 kamar yadda jaridar Daily Trust da ake wallafawa a Najeriyar ta rawaito.

Ɗaya daga cikin majiyoyin da ya buƙaci sakaya sunansa ya shaida wa manema labarai cewa, mayaƙan na Boko Haram sun kuma yi garkuwa da wasu sojojin na Najeriya bayan sun raba su da muhallansu a yayin farmakin.

ISWAP ta karɓe iko da Marte, sun kashe wani adadi na sojoji, sun kuma yi garkuwa da wasu, wasu da dama sun tsere zuwa Dikwa, kuma yanzu haka suna samun mafaka a sansanin runduna ta 24 da ke Dikwa

Ƴanta’addar sun kona tankunan yaƙi tare da awon gaba da tarin makamai daga sansanin sojin a cewar majiyar tsaron.

Ƙaramar Hukumar Marte dai, na da tazarar kilomita 38 daga Ƙaramar Hukumar Dikwa a jihar Borno da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya

Wata majiya a Dikwa ta shaida wa Daily Trust cewa, an jiyo ƙarar harbe- harbe

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp