Home General Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur...

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan bada jimawa ba al’umma Najeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.

Dangote ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke ganawa da manema labarai, a lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa ta dala biliyan 20, da ke yankin Lekki a jihar Lagos.

Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.

A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya bamu ƙarin makamashi, ina mai sheda muku cewa nan bada jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba ka ɗai.

A watan Oktoban bara ne dai matatar man Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a Najeriya.

To sai dai dillalan man fetur a Najeriya, na ganin ya kamata matatar Dangoten ta rinƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp