Home General Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur...

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya ce nan bada jimawa ba al’umma Najeriya za su ga gagarumin sauyi a ɓangaren man fetur ɗin ƙasar.

Dangote ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke ganawa da manema labarai, a lokacin da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya ziyarci matatar mansa ta dala biliyan 20, da ke yankin Lekki a jihar Lagos.

Ya ce sauyin da al’umma za su gani a yanzu, ba wai na rage farashin man ba ne, wanda zai sauya baki ɗaya yadda ake gudanar da harkokin mai ne a ƙasar.

A yanzu da shugaban ƙasa ya ziyarcemu, kuma ya bamu ƙarin makamashi, ina mai sheda muku cewa nan bada jimawa ba za ku ji daga garemu, kuma zai kasance sauyi ne a ɓangaren mai baki ɗaya a ƙasar, ba wai kawai rage farashinsa ba ka ɗai.

A watan Oktoban bara ne dai matatar man Dangote ta fara saida man fetur, lamarin da ya kawo saukar farashinsa a Najeriya.

To sai dai dillalan man fetur a Najeriya, na ganin ya kamata matatar Dangoten ta rinƙa saida lita ɗaya ƙasa da Naira ɗari 8, la’akari da cewar ana sayar wa kamfanin ne da ɗanyen mai a kuɗin Naira maimakon dalar Amurka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp