Home General Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabi ga al’ummar ƙasar da misalin ƙarfe 7 na safe a ranar Alhamis domin bikin ranar Dimokuraɗiyya ta shekarar 2025.

Cikin wata sanarwa da kwamitin shirya bikin ranar Dimokradiyyar ya fitar, ya ce da rana kuma Tinubu zai halarci zaman haɗin gwiwa da ƴan majalisar dokokin ƙasar.

Sai dai sanarwar ta bayyana cewa ba za a gudanar da taron faretin ranar ba a bana. A maimakon haka, za a gudanar da muhawarar jama’a a ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa da ƙarfe 4 na yamma.

Bikin na bana na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke cika shekara 26 ƙarƙashin mulkin dimokradiyya ba tare da katsewa ba tun bayan kawo ƙarshen mulkin soja a 1999.

A baya ana bikin ranar dimokradiyya a ranar 29 ga Mayu, wadda ke zama ranar rantsar da shugabannin ƙasa da gwamnoni da kuma ƴan majalisar tarayya da na jihohi.

Amma daga shekarar 2018, an sauya ranar zuwa 12 ga Yuni domin girmama zaɓukan 1993 da aka soke – da MKO Abiola ya lashe – zaɓen da ake ganin mafi sahihanci a tarihin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp