Home Labarai Matatar Dangote ta rage farashin Man fetur

Matatar Dangote ta rage farashin Man fetur

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur daga Naira 880 zuwa N840 kowace lita.

Kakakin Rukunin kamfanoni Dangote, Anthony Chiejina, ya tabbatar wa da jaridar PUNCH cewa an rage farashin a daren ranar Litinin.

Ya ce sabon farashin ya fara aiki ne a ranar 30 ga watan Yuni.

“An rage farashin man daga N880 zuwa N840 kowace lita daga 30 ga watan Yuni,” Chiejina

Idan za a iya tunawa matatar man Dangote ta kara farashin man fetur zuwa naira 880 a daidai lokacin da rikici ya barke tsakanin Isra’ila da Iran na tsawon kwanaki 12, lamarin da ya sa farashin danyen mai ya Karye akan dala 80 kan kowacce ganga.

jaridar PUNCH ta ruwaito cewa ‘yan kasuwar sun yi hasashen za a iya kara farashin daga ranar Litinin.

Abokan huldar matatar Dangote irinsu MRS, Heyden da AP ana sa ran za su rage farashin na su nan ba da jimawa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp