Home General Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje da dama a Filato

Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje da dama a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar hukumar Bokkos na jihar Filato, inda suka hallaka mutum biyu tare da ƙona gidaje da kuma coci-coci.

An kai harin ne da tsakar dare ɗauke da manyan makamai waɗanda suka zarta na ƙungiyar ƴan sintiri da ke yankin.

Shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasun Fudang ya bayyana mutane biyun da aka kashe ma’ikata ne a wani coci, inda ya ce an kuma ƙona gidaje da dama da kuma coci-coci, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Fudang ya ce maharan sun kuma lalata gonaki sannan suka yi awon gaba da shanu da tumakai da awakai da agwagi har ma da abincin da aka adana.

“Sun zo ne ta hanyar Ding’ak da Kopmur duk da cewa akwai shingen binciken jami’an tsaro a wajen. Sojoji sun yi harbi a iska sai dai ba su fafata da maharan ba,” kamar yadda Fudang ya yi zargi.

Shugaban al’ummar ta Bokkos ya ce harin na zuwa ne kwanaki biyu da kai irin makamancinsa a al’ummar Ndimar – Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da kuma ta jihar da su kai musu ɗaukin gaggawa tare da ganin an hukunta waɗanda ke far musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp