Home Labarai Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala...

Amurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

Ma’aikatar harkokin tsaron Amurkar ta ce gwamnatin kasar ta amince ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346

gwamantin kasar ta ce makaman da za a sayar wa Najeriyar sun haɗa da manyan bama-bamai da kuma rokoki, wanda sayar da makaman zai ƙara inganta ɓangaren tsaron Najeriya da kuma taimakawa tsarin harkokin wajen ta a yankin kudu da Hamadar Saharar Afirka.

“Cikin makaman har da wasu rokoki na zamani sama da 5,000,” in ji sanarwar Washington.

A 2014 lokacin mulkin Barack Obama, Amurka ta ki amincewa ta sayar wa Najeriya wasu muggan makamai, bayan nuna damuwa kan zargin sojojin ƙasar da take hakkin ɗan’adam.

A lokacin, gwamnatin Najeriya ta yi ƙorafin cewa hakan na yin cikas a yaƙi da take yi da masu tayar da kayar baya a arewa maso gabashin kasar.

Har zuwa yau, Nijeriya na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro da suka haɗa da hare-hare da ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi ke kai wa da kuma ayyukan masu garkuwa da mutane a arewa maso yamma da kuma ƴan awaren Biafra a kudu maso gabashin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp