Home Labarai Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi Alhinin mutuwar sheik Dahiru Bauchi

Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi Alhinin mutuwar sheik Dahiru Bauchi

Gwamnonin arewacin Najeriya sun nuna alhinin su bisa rasuwar jagoran ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya Shiekh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a yau alhamis.

Gwamnan jihar Gombe Muhammad Inuwa Yahaya, wanda shi ne shugaban ƙungiyar ta gwamnonin jihohin arewa, ya bayyana Shehin a matsayin malamin da rayuwarsa da koyarwarsa suka taɓa rayukan miliyoyin mutane a tsawon shekaru.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnatin jihar Gombe Uba Misili ya fitar, Gwamnan ya ce Sheikh Dahiru Bauchi ya sadaukar da rayuwarsa ta tsawon shekara 100 wajen yaɗa ilimin addinin musulunci, inda ya taimaka wajen koyar da karatun al Qurani da Hadisi da fiqihu da sauran karatuka.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewacin Najeriyar ya kuma ce malamin ya taka muhimiyyar rawa wajen samar da zaman lafiya,da juriya, da haɗin kai da kuma tarbiyya a tsawon rayuwarsa.

Ya kuma miƙa ta’aziyyar ɗaukacin gwamnonin arewacin Najeriya ga iyalan marigayin, da mabiya ɗariƙar Tijjaniyyah, da ma alummar musulmi kan gagarumin rashin da aka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp