Home Labarai Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Amnesty ba bukaci a gaggauta sakin Muhuyi Magaji

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty international tayi Allah wadai da abin da ta kira tauye hakkin dan adam da rundunar ‘yan sanda Nijeriya ke ci gaba da yiwa tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da karbar korafe korafe ta jihar Kano Muhuyi magaji Rimin Gado.

Ta cikin wani sautin murya da shugaban hukumar gudanarwa ta kungiyar ya aikewa PRNigeria Hausa, ya bayyana cewa kungiyar ta yi tofin alatsine kan yadda ake ci gaba da musgunawa gami da tauyi hakkin Muhuyi duk dace doka bata bawa ‘yan sandan damar kama shi ba, haka kuma babu wata kotu da ta bada umarnin yin kamun.

Kungiyar ta bukaci rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta gaggauata sakin Muhuyi tare kuma da daina cin zarafinsa da sauran Al’ummar Nijeriya.

Ba dai wannan ne karon barko da dakarun ‘yan sandan ke yiwa Muhuyi wannan kamu ba, duk da cewa ana kallon hakan na da nasaba da takun saka da yake fuskanta da wasu ‘yan siyasa a jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp