Home Labarai Majalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatar

Majalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatar

Majalisar dattawa ta amince da naɗin mutum uku na farko da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata domin tantancewa a matsayin jakadun Najeriya a ƙasashen waje.

Sabbin jakadun da majalisar ta amince da naɗin nasu su ne Aminu Muhammad Dalhatu daga Jihar Jigawa, Lateef Kayode Kolawole Are daga Jihar Ogun, da kuma Emmanuel Ayodele Oke, CFR, daga Jihar Oyo.

Majalisar ta amince da naɗin ne bayan la’akari da rahoton kwamitin majalisar dattawa kan harkokin waje, wanda ya gudanar da tantancewar waɗanda aka gabatar a makon da ya gabata.

Sai dai har yanzu akwai ragowar wasu 64 da shugaba Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa, waɗanda aka tantance amma ba a kai ga tabbatar da naɗin nasu ba.

Shugaba Tinubu ya tura sunayen waɗannan jakadu uku ne a ranar 26 ga Nuwamba.

Wannan shine jerin sunaye na farko na jakadu da Shugaban ƙasa ya miƙa wa Majalisar Dattawa tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp