Home Labarai Majalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatar

Majalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatar

Majalisar dattawa ta amince da naɗin mutum uku na farko da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata domin tantancewa a matsayin jakadun Najeriya a ƙasashen waje.

Sabbin jakadun da majalisar ta amince da naɗin nasu su ne Aminu Muhammad Dalhatu daga Jihar Jigawa, Lateef Kayode Kolawole Are daga Jihar Ogun, da kuma Emmanuel Ayodele Oke, CFR, daga Jihar Oyo.

Majalisar ta amince da naɗin ne bayan la’akari da rahoton kwamitin majalisar dattawa kan harkokin waje, wanda ya gudanar da tantancewar waɗanda aka gabatar a makon da ya gabata.

Sai dai har yanzu akwai ragowar wasu 64 da shugaba Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa, waɗanda aka tantance amma ba a kai ga tabbatar da naɗin nasu ba.

Shugaba Tinubu ya tura sunayen waɗannan jakadu uku ne a ranar 26 ga Nuwamba.

Wannan shine jerin sunaye na farko na jakadu da Shugaban ƙasa ya miƙa wa Majalisar Dattawa tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp