Home Labarai Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Nigerian Army

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Haɗin Kai daƙile yaƙunrin hain ƴanbindiga ina sun kashe su daga tsaunukan Mandara a lokacin da suka yunƙurin kai hari a cikin al’ummar Bitta da ke Borno.

Rundunar ce ta sanar da hakan a shafinta na X inda ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 12:30 na tsakar daren ranar 18 ga Disamba, 2025 lokacin da sojojin suka gano wannan yunƙuri na ‘yanbindig da ke tafiya zuwa yankin.

A cewar rundunar, sai da sojojin suka bari ƴanbindigar suka shiga wani yanki da aka musu tarko kafin buɗe musu wuta, inda suka kashe wasu daga cikin maharan, ciki har da wani kwamandansu da mai ɗaukar musu hoto.

Rundunar ta ƙara da cewa, daga baya rundunar sojojin sama ta Operation Haɗin Kai ta kai farmaki kan waɗanda suka tsere lamarin da ya ƙara hallaka wasu tare da tarwatsa hanyoyin gudunsu.

A lokacin da ake fafatawa a yankin, an ruwaito cewa sojoji sun bi diddigin hanyoyi da dama, kuma sun gano kaburbura marasa zurfi, wanda ke nuna ƙarin asarar rayuka da aka yi wa ‘yan ta’addan a lokacin fafatawar.

Bayan fafatawar, sojoji sun gudanar da bincike a yankin inda suka ƙwato kayayyaki da makamai da dama.

Rundunar ta ce sojoji na ci gaba da ayyukansu domin hana masu ta da ƙayar baya samun damar kai hari, tare da tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp