Home DUNIYA Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

Food

Yaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaru

 

Hauhawar farashi a Najeriya ya ƙaru sosai a watan Maris a karon farko cikin wannan shekara, kamar yadda alƙaluma daga hukumar ƙididiga ta ƙasar suka nuna.

Ana ganin lamarin zai ƙara haifar da cikas ga gwamnatin ƙasar ƙarƙashin Bola Ahmed Tinubu a daidai lokacin da ake tunkarar zaɓukan 2027 a watan Junairun baɗi.

Ƙasar wadda ta fi kowace ƙasa yawan al’umma a Afrika na ta ƙokarin rage hauhawar farashi kafin a fara yaƙin Iran, inda gwamnatin ke ta ɗaukar matakai da dama a cikin watanni 11 da suka gabata.

Sai dai yaƙin Gabas ta Tsakiya ya mayar da hannun agogo baya musamman sakamakon tashin farashin man fetur, inda ya shafi farashin kayan masarufi.

Hukumar NBS a ƙasar ta ce hauhawar farashi ta ƙaru daga 15.06% a watan Fabrairu zuwa 15.38% a watan Maris.

Hauhawar farashin kayan abinci kuma ta ƙaru daga 12.12% zuwa 14.31%

Wasu al’ummar ƙasar sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa hauhawar farashin da ake samu a Najeriya na ƙara jefa rayuwarsu cikin matsi da ƙunci.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp