Masu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno
AƘalla mutum 11 aka bayar da rahoton masu iƙirarin jihadi sun kashe a wasu ƙauyukan jihar Borno da ke arewacin Najeriya a ranar Asabar.
Read Also:
Wata ƙungiya mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi a jihar Borno ta ce an kashe wasu manoma bakwai a yayin da suke shuka a gonakinsu.
Haka ma rahotonni sun ce an kashe wasu manoman huɗu a yankin tafkin Chadi.
Asusun bayar da lamuni na duniya ya yi gargaɗin cewa rikicin zai iya durƙusar da harkokin noma, lamarin da ka iya ƙara yaɗuwar talauci tsakanin al’umomin yankin.











