Home SIYASA Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

 

Jam’iyyar PDP tsagin Tanimu Turaki ta nuna damuwa kan hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta yanke kan soke rijistar jam’iyyar NDC, inda ta ce hakan koma baya ga dimokuraɗiyya a Najeriya.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na riƙo, Ini Ememobong, ya fitar, PDP ta ce ko da yake tana jiran samun cikakken bayani dangane da hukuncin kotun, ta yi alawadai da abin da ta kira “murƙushe dimokuraɗiyya” a ƙasar.

Jam’iyyar ta ce hukuncin ya zo ne bayan ƴan Najeriya da dama sun kashe kuɗaɗe domin neman muƙaman siyasa a ƙarƙashin NDC.

“Wannan hukunci ba wai yana takaita tsarin jam’iyyu ba ne kawai, yana haifar da asara ga ƴan Najeriya da suka sa rai a jam’iyyar,” in ji sanarwar.

PDP ta kuma zargi gwamnatin ƙasar ƙarƙashin jam’iyyar APC da ƙoƙarin dakushe jam’iyyun adawa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, domin bai wa Tinubu damar sake tsayawa takara ba tare da wani ƙalubale.

Jam’iyyar ta buƙaci shugabannin NDC su ƙalubalanci hukuncin a kotun ɗaukaka ƙara, tare da kira ga gwamnatin tarayya da ta daina abin da take yi domin zaman lafiya da kuma tabbatar da dorewar dimokuraɗiyya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp