Home SIYASA Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

 

Jam’iyyar PDP tsagin Tanimu Turaki ta nuna damuwa kan hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta yanke kan soke rijistar jam’iyyar NDC, inda ta ce hakan koma baya ga dimokuraɗiyya a Najeriya.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na riƙo, Ini Ememobong, ya fitar, PDP ta ce ko da yake tana jiran samun cikakken bayani dangane da hukuncin kotun, ta yi alawadai da abin da ta kira “murƙushe dimokuraɗiyya” a ƙasar.

Jam’iyyar ta ce hukuncin ya zo ne bayan ƴan Najeriya da dama sun kashe kuɗaɗe domin neman muƙaman siyasa a ƙarƙashin NDC.

“Wannan hukunci ba wai yana takaita tsarin jam’iyyu ba ne kawai, yana haifar da asara ga ƴan Najeriya da suka sa rai a jam’iyyar,” in ji sanarwar.

PDP ta kuma zargi gwamnatin ƙasar ƙarƙashin jam’iyyar APC da ƙoƙarin dakushe jam’iyyun adawa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, domin bai wa Tinubu damar sake tsayawa takara ba tare da wani ƙalubale.

Jam’iyyar ta buƙaci shugabannin NDC su ƙalubalanci hukuncin a kotun ɗaukaka ƙara, tare da kira ga gwamnatin tarayya da ta daina abin da take yi domin zaman lafiya da kuma tabbatar da dorewar dimokuraɗiyya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar Sokoto
X whatsapp