Home SIYASA Kotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu...

Kotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4

inec

Kotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4

Wata babbar Kotun Tarayyar Najeriya ta umurci hukumar zaɓen ƙasar INEC ta soke rajistar jam’iyyar adawa ta ADC da wasu jam’iyyu huɗu.

Kotun da ke Abuja ta ce jam’iyyun sun gaza cika sharuɗan da kundin tsarin mulkin kafa jam’iyyun siyasa.

Mai Shari’a Peter Lifu ne ya yanke hukuncin, inda ya ce jam’iyyun ba su samu kashi 25 cikin 100 na ƙuri’un da doka ta tanada a zaɓukan da suka gabata ba.

Jam’iyyun da hukuncin ya shafa su ne ADC, Accord, AA, APP da ZLP. Ya bayyana cewa jam’iyyun taka sashe na 225 na kundin tsarin mulkin Najeriya.

Kotun ta kuma umarci INEC da kada ta bari jam’iyyun su shiga zaɓuka masu zuwa, ciki har da babban Zaɓen 2027, matuƙar ba su cika sharuɗan da doka ta tanada ba.

Wata ƙungiyar tsofaffin ƴan majalisa ta shigar, inda ta yi zargin cewa jam’iyyun sun kasa cika ƙa’idojin da suka shafi samun goyon baya da kuma sakamakon zaɓe.

Sai dai jam’iyyar ADC ta fitar da sanarwar cewa za ta shiga zaɓen 2027 kuma tana kira ga mabiyanta da su yi watsi da hukuncin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp