Home Labarai Shin da Gaske Tsohon Sarki Sanusi II Zai Kawo Ziyara Jahar Kano...

Shin da Gaske Tsohon Sarki Sanusi II Zai Kawo Ziyara Jahar Kano ?

Shin da Gaske Tsohon Sarki Sanusi II Zai Kawo Ziyara Jahar Kano ?

Manyan masu ruwa da tsaki da masanan tsaro sun bayyana damuwarsu game da jita-jitar tsohon Sarki zai kai ziyara jihar Kano.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa a halin yanzun ba ta da masaniya kan lamarin, idan ma dagaske ne ta na maraba da zuwansa.

Ana gani abubuwa da dama ka iya ta da zaune tsaye tsakanin al’ummar Kano, matukar Sanusi II ya shigo jihar kano.

Kano – Masana a siyasa da tsaro sun nuna matukar damuwarsu kan shirin tsohon sarkin da aka sauke, Sanusi Lamido, na kai ziyara jahar Kano.

Wasu daga cikin masu ruwa da tsaki na jiha, waɗan da suka zanta da jaridar Leadership, sun roki tsohon sarkin ya dakatar da shirin zuwa Kano a halin yanzu.

A cewarsu, tsoron da suke shi ne, akwai yuwuwar tada hankulan mutane wanda ka iya sanadin rikici tsakanin masoyan tsohon sarkin da yan adawarsa.

Ɗaya daga cikin manyan mutane, kuma babban jami’in tsaro, wanda ya nemi a sakaya sunansa yace ra’ayin tsohon sarkin na kai takara Kudu ya fusata wasu kuma zasu iya amfani da zuwansa don tada rikici.

Kazalika ya ƙara da cewa duk da sanin kowa ne an tunɓuke shi daga Sarauta, amma yana halartar taruka cikin kayan Sarauta, hakan ka iya jawo matsala saboda akwai Sarki mai ci a Kano.

Ya ce:

“Kowa ya san cewa Sanusi tsohon ɗalibin Kwalejin Legas ne, kuma yana da abokan da suka yi makaranta tare a kudu maso yamma, amma har yanzun ba’a san wanda yake goyon bayan ya gaji Buhari daga yankin ba.”

“Kazalika sanin kowa ne Sanusi ya bayyana cewa ya fi son rike muƙamin Khalifan Ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya, fiye da shiga neman kujerar siyasa.”

Shin gwamnatin Kano ta san da zuwan tsohon sarkin?

A ɓagaren gwamnati, Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Malam Muhammad Garba, yace ba shi da masaniya kan shirin zuwan Sanusi.

Ya ƙara da cewa idan ma jita-jitar gaskiya ce, “Muna maraba da shi, a matsayinsa na.ɗan asalin jihar Kano, yana da damar zuwa jiharsa, gwamnati ba ta da matsala da haka.”

Tsohon hadimin Sanusi, Farfesa Auwal Hamisu Yadudu, ya bayyana cewa ba shi da masaniyar zuwan tsohon sarkin Kano.

Farfesa Yadudu yace:

“Ban san zai shigo jihar Kano ba, ba wanda ya sanar da ni wannan shirin, kuma ina da yaƙinin cewa idan zai shigo ina daga cikin waɗan da za’a gaya wa.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp