Home Taska ‘Yan Sanda Sun Ceto Mutane 20 da ‘Yan Bindiga Suka yi Garkuwa...

‘Yan Sanda Sun Ceto Mutane 20 da ‘Yan Bindiga Suka yi Garkuwa da su a Jahar Neja

‘Yan Sanda Sun Ceto Mutane 20 da ‘Yan Bindiga Suka yi Garkuwa da su a Jahar Neja

 

‘Yan sandan Neja sun ceto mutum 20 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su sakamakon samamen da suka kai kan sansanin ‘yan fashin daji a jihar da ke tsakiyar Najeriya.

Kakakin rundunar a Neja, DSP Wasiu A. Abiodun, ya faɗa cikin wata sanarwa ranar Lahadi cewa dakarunsu sun kai samamen ne a yankin Anaba da ke Ƙaramar Hukumar Magama.

Bayan fafatawa gami da harbe-harbe tare da ‘yan bindigar, dakaru sun yi nasarar kashe ‘yan fashin tare da ƙwato shanun da suka sata.

“Ƙarin dakarun da aka tura ciki har da sojoji da ‘yan banga sun fara fafatawa da ‘yan bindigar a kan hanyar shanu da Ibeto kusan tsawon awa biyu a lokacin da maharan ke ƙoƙarin guduwa,” in ji shi.

Daga cikin makaman da aka ƙwace daga hannunsu sun haɗa da bindigar AK-47 ɗaya da ƙunshin harsasai 30 da wayar salula bakwai da babur ɗaya, a cewar DSP Abiodun.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp