Home Taska Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya

Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya

Gobara ta Tashi a Harabar Cibiyar Horar da Lauyoyi ta Najeriya 

 

An samu tashin gobara a daren ranar Laraba, 16 ga watan Fabrairu, a harabar cibiyar horar da lauyoyi ta Nigerian Law School dake kan titin Ozumba Mbadiwe a Victoria Island da ke jahar Legas.

Majiyoyin da suka zanta da ‘yan jarida sun bayyana cewa, lamarin ya haifar da tarzoma da tashin hankali a yankin.

TheCable ta ruwaito cewa, an nakalto daga majiya mai tushe a ranar Alhamis, 17 ga watan Fabrairu cewa gobarar ta tashi ne a sakamakon matsalar wutar lantarki da aka samu a cibiyar.

Duk da haka, an kashe gobarar cikin kankanin lokaci.

Majiyar ta ce:

“An samu tashin gobara jiya da daddare, amma nan take aka shawo kan ta. Gobarar ta faru ne sakamakon lalacewar wutar lantarki.”

A cewar Vanguard, kimanin mutane biyar da gobarar ta shafa sun kwanta a asibiti a halin yanzu.

Rahoton ya ce:

“Gobarar ta zo da wani kara. An samu turmutsutsu a dakin kwanan dalibai. Na ga wani dalibin da ya yi tsalle daga bene na farko inda gobarar ta tashi kusa da dakin karatu. Wasu daliban sun fice daga dakunansu a firgice.

“Akalla, mutane biyar sun samu munanan raunuka yayin da wata tsohuwa mace mai aikin shara ta samu gurdewa a yatsar kafa.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp