Home Taska Sojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa

Sojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa

Sojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa

Rahotanni a Najeriya sun ce sojojin Najeriya sun halaka wasu kwamandojin Iswap a Sambisa ciki har da wanda ake kira Amir Buba Danfulani wanda ake zargin ya shigar da fulani makiyaya ƙungiyar.

A cikin rahoton da ta fitar, jaridar PRNigeria da ke da kusanci da rundunar sojin Najeriya ta ce an yi wa mayaƙan ne luguden wuta ta sama a wasu sansanoninsu da kuma dajin Sambisa a arewa maso gabashin Najeriya, kamar yadda majiyoyin soji suka tabbatar.

Sai dai babu wata sanarwa kawo yanzu daga rundunar sojin Najeriya da ke tabbatar da al’amarin.

Rahotannin sun ce an yi wa mayaƙan ne ruwan rokoki a Tumbun Kaiyowa da kuma Tumbun Allura, tare da kashe mayaƙan.

An kuma yi wa mayaƙan ruwan wuta ta sama a dajin Sambisa. Kwamandojin Iswap da aka kashe sun hada da Musa Amir Jaish da Mahd Maluma da Abu-Ubaida da Abu-Hamza da kuma Abu-Nura umarun Leni, a cewar PRNigeria.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp